fidelitybank

Burkina Faso da Mali tare da Nijar na son zama dunƙulalliyar ƙasa

Date:

Gwamnatocin soji a ƙasashen Nijar, da Burkina Faso, da Mali sun bayar da shawarar kafa ƙasa ta tarayya da za ta haɗa ƙasashen uku na Afirka ta Yamma kuma maƙwabtan juna.

Sun bayyana shawarar ce bayan ganawar da ministocin harkokin wajensu suka yi a birnin Bamako na Mali a ƙarshen makon nan.

Lamarin na zuwa ne yayin da Nijar da Burkina Faso ke son bin sawun Mali na ficewa daga ƙungiyar ƙasashen G5, wadda aka kafa don yaƙar masu iƙirarin jihadi a yankin Sahel.

Wata sanarwar bayan taron ministocin ta ce ƙasashen sun bayyana “babban yunƙurinsu na zaman lafiya, da cigaba, da kuma difilomasiyya” da kafa ƙasar zai samar.

“Ministocin…da ke da burin haɗe Burkina Faso, da Mali, da Nijar sun bai wa shugabannin ƙasashen shawarar kafa ƙasa ta tarayya mai suna Alliance of Sahel States,” a cewar sanarwar. Alliance of Sahel States na nufin Ƙasashen Ƙawance na Sahel.

Ƙungiyar raya tattalin arzikin Afirka ta Yamma Ecowas ta dakatar da ƙasashen uku daga cikinta bayan sojoji sun hamɓarar da gwamnatocin farar hula a ƙasashensu

legit ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp