Tsohon shugaban hafsun sojoji na kasa, Laftanan Janar Tukur Yusuf Buratai (mai ritaya), ya nesanta kansa daga neman takarar shugaban kasa a 2023.
Jakadan Najeriya a kasar Benin, ya bayyana cewa, bai fadawa kowa ya na neman mulki ba, a cewar, Jaridar Vanguard.
Hakan na zuwa ne bayan fastocin tsohon sojan sun fara yawo, a na jita-jitar zai yi takara a zaben 2023.
Hankalin Jakadan Najeriya zuwa Jamhuriyyar Nijar, kuma tsohon shugaban hafsun sojojin kasa, Laftanan Janar Tukur Yusuf Buratai ya zo ga kiraye-kiraye da fastoci da wasu ke yadawa, su na kiran shi ya shiga siyasa, ya nemi takarar shugaban kasa.