Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya yi alhinin rasuwar mutane uku da wasu shida da suka samu raunuka da dama a wani hatsarin mota da ya afku a hanyar Potiskum zuwa Bauchi.
Gwamna Buni a wata sanarwa da mai magana da yawun sa, Mamman Mohammed ya fitar a ranar Lahadin da ta gabata ya bayyana hatsarin a matsayin abin ban tsoro.
“Mutuwar da aka samu da raunukan sun kasance masu matukar tayar da hankali, amma wannan lokaci ne da aka ayyana da yardar Allah,” in ji shi.
Karanta Wannan:Â Buni ya roki CBN ya kara wa’adin karbar tsofaffin kudi
Buni ya yi addu’ar Allah ya gafarta musu kurakurensu, ya jikan su da Aljannar Firdausi, da iyalansu, ya kuma baiwa iyalansu hakurin jure rashin.
Ya kuma yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka samu raunuka daban-daban da ke barazana ga rayuwarsu cikin gaggawa.
Hakazalika, Gwamna Buni ya jajantawa wadanda bala’in gobara ya rutsa da su a unguwar Sabon Pegi a cikin birnin Damaturu.
Gwamna Buni ya bayyana lamarin da ya shafi wasu shaguna a matsayin abin bakin ciki da takaici.