Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya amince da daukar ma’aikata 196 da suka kammala karatu a kwalejin kimiyya da fasaha ta Nguru, domin bunkasa ma’aikata a fannin lafiya.
A wata sanarwa da Babban Daraktan Yada Labarai na gwamnan jihar, Alhaji Mamman Mohammed Buni ya fitar, ya ce, samar da ayyukan yi ga daliban kwalejin su 196 zai samar da kwararrun da ake bukata a cibiyoyin lafiya a fadin jihar.
Ya bayyana cewa daga cikin wadanda aka amince da daukar aiki akwai kwararrun a fannin magunguna da kwararrun masu aiki a dakin gwaje-gwaje da kwararrun likitocin hakori da kwararrun masu kula da bayanan lafiya.
Gwamna Buni ya lura da cewa, amincewar ta shafi 23 kwarwarru a fannin hada magunguna, 60 daga dakin gwaje-gwaje, 62 daga bangaren hakori da 51 Kwararrun Gudanar da Bayanan Lafiya.
Ya kuma bukaci wadanda suka ci gajiyar shirin da su jajirce wajen yin aiki tare da kuma hidimtawa jama’a cikin mutunci.
Gwamnatin Buni ta kafa aƙalla cibiyoyin kiwon lafiya guda ɗaya a cikin kowane gundumomin siyasa 178 da ke faɗin jihar, ta kafa ƙarin asibitocin da ƙwararrun asibitoci domin haɓaka aikin kiwon lafiya a jihar.