fidelitybank

Buni ya dauki ma’aikata 196 a fannin lafiya

Date:

Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya amince da daukar ma’aikata 196 da suka kammala karatu a kwalejin kimiyya da fasaha ta Nguru, domin bunkasa ma’aikata a fannin lafiya.

A wata sanarwa da Babban Daraktan Yada Labarai na gwamnan jihar, Alhaji Mamman Mohammed Buni ya fitar, ya ce, samar da ayyukan yi ga daliban kwalejin su 196 zai samar da kwararrun da ake bukata a cibiyoyin lafiya a fadin jihar.

Ya bayyana cewa daga cikin wadanda aka amince da daukar aiki akwai kwararrun a fannin magunguna da kwararrun masu aiki a dakin gwaje-gwaje da kwararrun likitocin hakori da kwararrun masu kula da bayanan lafiya.

Gwamna Buni ya lura da cewa, amincewar ta shafi 23 kwarwarru a fannin hada magunguna, 60 daga dakin gwaje-gwaje, 62 daga bangaren hakori da 51 Kwararrun Gudanar da Bayanan Lafiya.

Ya kuma bukaci wadanda suka ci gajiyar shirin da su jajirce wajen yin aiki tare da kuma hidimtawa jama’a cikin mutunci.

Gwamnatin Buni ta kafa aƙalla cibiyoyin kiwon lafiya guda ɗaya a cikin kowane gundumomin siyasa 178 da ke faɗin jihar, ta kafa ƙarin asibitocin da ƙwararrun asibitoci domin haɓaka aikin kiwon lafiya a jihar.

nigeria legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...
X whatsapp