fidelitybank

Buni ya baiwa ‘ya’yan Malamin addinin musulunci da aka kashe aikin yi

Date:

Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya baiwa ‘ya’yan marigayi malamin addinin musulunci, Sheikh Goni Aisami, aikin yi a gwamnain sa.

Gwamna Buni ya ba da umarnin ne a ranar Talata lokacin da ‘yan uwa suka ziyarce shi, domin nuna jin dadinsu kan yadda ya ke nuna damuwarsa ga iyalan.

Gwamna Buni ta bakin mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Mamman Mohammed ya tabbatar da cewa gwamnati za ta tabbatar da gudanar da bincike kan lamarin mutuwar malamin.

Ya kuma ba da tabbacin gwamnati za ta ci gaba da tallafa wa ‘yan uwa domin ta yi asarar abin da za su ci.

Malam Ibrahim Aisami, wanda ya yi magana a madadin ‘yan uwa, ya nuna jin dadinsa da sakon ta’aziyya da ziyarar da wata babbar tawagar gwamnati ta kai domin jajantawa iyalan.

Ya ce aikin zai rage wa iyalansu wahala sakamakon rasuwar malamin.

A ranar Juma’ar da ta gabata ne wasu mutane biyu da ake zargin sojoji ne suka kashe Sheikh Aisami.

A halin da ake ciki dai, ‘yan sanda sun kama wadanda ake zargin yayin da rundunar sojin ta sanar da cewa ta fara gudanar da bincike kan lamarin domin bayyana cikakken bayani kuma duk wanda aka samu yana so zai fuskanci shari’a.

nnn hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp