Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Sanata Bukola Saraki, zai gana a yau da Sanatocin PDP.
Saraki ya kasance shugaban majalisar dattawa ta takwas tsakanin 2015 zuwa 2019.
Sanarwar ganawar da Saraki ya yi da ‘yan majalisar dattawan PDP na kunshe ne a cikin wata wasika mai dauke da sa hannun shugaban marasa rinjaye, Enyinnaya Abaribe.
Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Omo-Agege, wanda ya jagoranci zaman majalisar a ranar Talata ya karanta wasikar.