fidelitybank

Buhari zai taron gaggawa a kan matsalar da ake fuskanta

Date:

Shugaba Muhammadu Buhari, zai jagoranci wani taron gaggawa na majalisar magabata a ranar Juma’a mai zuwa 10 ga watan nan na Fabrairu, ranar da aka sanya wa’adin daina amfani da wasu daga cikin manyan takardun kudi.

Taron zai tattauna ne a kan matsalolin da kasar ke fama da su a yanzu da suka hada da karancin man fetur da na kudin kasar Naira da matsalar tsaro yayin da kasar ke fuskantar babban zabenta da za a fara ranar 25 ga watan nan nan Fabrairu wato kasa da sati uku daga yanzu.

Karanta Wannan: Arewa ce ya kamata ta gaji Buhari – Dogara

Halin da kasar ke ciki na wadannan matsaloli musamman karancin Naira da kuma matsalar mai sun sa an fara zanga-zanga a wasu sassan kasar da dama.

Jaridar Daily Trustt ta ruwaito cewa, ana sa ran gwamnan Babban Bankin Najeriyar, Godwin Emefie zai yi wa majalisar bayani a yayin taron da zai gudana a fadar shugaban kasar, da ke Abuja, game da batun canjin kudin ksara, lamarin da ya jefa al’umma da dama cikin halin kaka-ni-kayi.

Haka kuma jaridar ta kara da cewa wasu kafofi na fadar shugaban sun gaya mata cewa shugaban hukumar zaben kasar, Farfesa Mahmood Yakubu, da shugaban ‘yan sanda na kasar Usman Alkali Baba za su yi wa majalisar bayani kan shirye-shiryen zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar tarayya da za a yi ranar 25 ga watan na Fabrairu da kuma na gwamnoni da ‘yan majalisar jiha da za a yi ranar 11 ga watan Maris.

Majalisar magabatan ta kunshi shugaban kasar da mataimakinsa da sakataren gwamnatin tarayya da tsofaffin shugabannin kasa da tsofaffin manyan alkalan kasa da shugaban majalisar dattawa da shugaban majalisar wakilai da gwamnonin jihohi 36 da kuma babban lauyan gwamnati kuma ministan shari’a.

legit new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaÉ—i masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga FalasÉ—inawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen É—an gwagwarmayar nan kuma É—an jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp