fidelitybank

Buhari zai taron gaggawa a kan matsalar da ake fuskanta

Date:

Shugaba Muhammadu Buhari, zai jagoranci wani taron gaggawa na majalisar magabata a ranar Juma’a mai zuwa 10 ga watan nan na Fabrairu, ranar da aka sanya wa’adin daina amfani da wasu daga cikin manyan takardun kudi.

Taron zai tattauna ne a kan matsalolin da kasar ke fama da su a yanzu da suka hada da karancin man fetur da na kudin kasar Naira da matsalar tsaro yayin da kasar ke fuskantar babban zabenta da za a fara ranar 25 ga watan nan nan Fabrairu wato kasa da sati uku daga yanzu.

Karanta Wannan: Arewa ce ya kamata ta gaji Buhari – Dogara

Halin da kasar ke ciki na wadannan matsaloli musamman karancin Naira da kuma matsalar mai sun sa an fara zanga-zanga a wasu sassan kasar da dama.

Jaridar Daily Trustt ta ruwaito cewa, ana sa ran gwamnan Babban Bankin Najeriyar, Godwin Emefie zai yi wa majalisar bayani a yayin taron da zai gudana a fadar shugaban kasar, da ke Abuja, game da batun canjin kudin ksara, lamarin da ya jefa al’umma da dama cikin halin kaka-ni-kayi.

Haka kuma jaridar ta kara da cewa wasu kafofi na fadar shugaban sun gaya mata cewa shugaban hukumar zaben kasar, Farfesa Mahmood Yakubu, da shugaban ‘yan sanda na kasar Usman Alkali Baba za su yi wa majalisar bayani kan shirye-shiryen zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar tarayya da za a yi ranar 25 ga watan na Fabrairu da kuma na gwamnoni da ‘yan majalisar jiha da za a yi ranar 11 ga watan Maris.

Majalisar magabatan ta kunshi shugaban kasar da mataimakinsa da sakataren gwamnatin tarayya da tsofaffin shugabannin kasa da tsofaffin manyan alkalan kasa da shugaban majalisar dattawa da shugaban majalisar wakilai da gwamnonin jihohi 36 da kuma babban lauyan gwamnati kuma ministan shari’a.

latest nigeria newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaÆ™i don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin Æ™era nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe Æ´an Æ™asarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta Æ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Æ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Æ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a Æ™yale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp