Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya nanata cewa, zai koma garin Daura na jihar Katsina bayan wa’adin sa ya cika.
Buhari ya bayyana haka ne ta bakin ministan yada labarai da al’adu Lai Mohammed.
Ya ce babu wata gwamnati da ta nuna rikon amana ga tsarin dimokuradiyya, kuma babu wani shugaban kasa tun 1999 da bai kai ga shugaban kasa Muhammadu Buhari ba, dangane da barin mulki bayan kundin tsarin mulki ya kayyade wa’adi biyu.
“Shugaba Buhari bai bar kowa a cikin shakkun karensa ba
aniyar tabbatar da sahihin zabe da gaskiya da mika mulki ga wanda ‘yan Najeriya suka zaba sannan kuma ya dawo Daura bayan ranar 29 ga watan Mayun 2023. A kwanakin baya ne a ranar Juma’ar da ta gabata, lokacin da ya ziyarci Sarkin Daura.
“Shugaba Buhari ya shaida wa Masarautar cewa zai dawo ya zauna a Daura bayan ya mika mulki a ranar 29 ga Mayu, 2023.
Ya kara da cewa Buhari ya kuma baiwa INEC goyon bayan da ba a taba ganin irinsa ba ta hanyar sanya hannu kan dokar zabe ta 2022.