fidelitybank

Buhari zai tafi Habasha taron ƙungiyar Tarayyar Afirka

Date:

Shugaba Muhammadu Buhari zai tashi daga Abuja zuwa Addis Ababa, babban birnin Habasha domin halartar taron ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU) karo na 36, a yau Alhamis.

A wata sanarwa da kakakin shugaban, Mallam Garba Shehu, ya fitar, ya ce, a yayin da yake birnin na Addis Ababa, Buhari zai halarci wasu manyan taruka uku, a kan tsaro da zaman lafiya da batun sauyin yanayi da kuma yanayin siyasar da ake ciki a wasu ƙasashen yammacin Afirka.

Sanarwar wadda ta bayyana taken taron a matsayin, hanzarta aiwatar da tsarin kasuwanci maras shinge na nahiyar Afirka, ta kuma bayyana cewa, shugaban zai halarci wani taro na musamman na shugabannin ƙasashen Afirka ta Yamma da za a yi a gefen babban taron na AU.

Kakakin ya ce, taro na farko da za a yi shi ne na kwamitin tsaro na shugabannin ƙasashen ƙungiyar a kan halin da ake ciki a gabashin Jamhuriyar Dumukuradiyyar Kongo, wanda shugaban Afirka ta Kudu zai jagoranta a matsayinsa na shugaban kwamitin a watan Fabarairu.

”Sai kuma taron kwamitin shugabannin ƙasashe da gwamnatoci a kan sauyin yanayi wanda shugaban Jamhuriar Nijar ke jagoranta,” in ji sanarwar

Shugaba Buharin wanda zai samu rakiyar wasu ministoci da wasu manyan jami’an gwamnati zai koma Najeriya ranar Litinin 20 ga watan nan na Fabarairu, kamar yadda sanarwar ta ce.

opra news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp