Shugaban kasa Muhammadu Buhari, zai rattaba hannu a kan kasafin kudin shekarar 2023 a ranar Talata mai zuwa.
Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmad Lawan ne ya bayyana haka ga manema labarai a ranar Juma’a, bayan wata ganawar sirri da ya yi da shugaban a fadar shugaban kasa da ke Abuja.
Lawan ya kuma bayyana cewa ya tattauna wasu batutuwan da suka shafi kasa da shugaban kasa, ciki har da tallafin da majalisa ke baiwa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) gabanin zaben 2023, da bukatar karin lamuni da Buhari ya nema da dai sauransu.
A cewar sa: “Muna sa ran shugaban kasa ya rattaba hannu a kan kasafin kudin shekarar 2023, da yardar Allah, ranar Talata.
“Wannan ya faru ne saboda mun rattaba hannu kan takardar a jiya, bayan da muka yi hasarar wani lokaci saboda wasu bata-gari da muka samu a cikin kudirin da aka gabatar wa Majalisar Dokoki ta kasa.
“Amma alhamdulillahi, NASS (Majalisar Tarayya) a majalisun biyu sun zartar da kasafin kudin shekarar 2023 a ranar Laraba.
“Kuma abu na farko a ranar Talata, na yi imanin cewa shugaban kasa zai rattaba hannu kan kasafin kudin 2023.”