Shugaba kasa Muhammadu Buhari, sauka a Jihar Ogun, domin ƙaddamar da wasu ayyuka da gwamnati ta gudanar a jihar.
Gidan talabijin na Channels ya rawaito cewa, a na sa ran Buhari zai ƙaddamar da sabuwar ƙofar shiga gari ta Ogun City Gate da kuma Titin Abeokuta zuwa Sagamu mai tsawon kilomita 42.
Sauran ayyukan sun ƙunshi rukunin gidaje biyu, ciki har da na marasa ƙarfi da ke Kobape, da wani mai suna Kings Court Estate duka a Abeokuta babban birnin jihar.
Bayan haka, a na sa ran shugaba Buhari, zai yi wata ganawa da mahukunta da kuma ‘yan jam’iyyar APC na jihar.