fidelitybank

Buhari yaki karbar kyautar Agogon lu’u-lu’u da jirgin sama – Garba Shehu

Date:

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Najeriya Muhammad Buhari, Mallam Garba Shehu, ya bayar da labarin yadda marigayin ya ƙi karɓar wasu kyautuka lokacin yana mulki, ciki har dakyautar jirgin sama.

Da yake magana ta cikin shirin Inside Sources na Channels TV, Garba Shehu ya ce Buhari ya ƙi amincewa da karɓar kyautar agogon lu’ulu’u wani ɗankasuwa a Najeriya ya ƙera da sunansa a jiki, da kuma kyautar jirgin sama da ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta yi masa tayi.

“Shugaban ƙasa ya kalli agogon, ya ce ‘Agogon lu’ulu’u? Ba zan iya saka wannan ba. Ku faɗa masa yana ƙoƙari…kuma za mu ci gaba da ƙarfafa masa gwiwa. Ya ci gaba da ɗaukaka sunan Najeriya, amma ku mayar masa da agogon nan. Ba zan iya amfani da shi ba.’,” kamar yadda Garba ya bayyana ranar Juma’a.

Ya kuma bayar da labarin ziyarar da Buhari ya kai birnin Dubai a 2016, inda shugaban ƙasar ya yi masa tayin kyautar jirgin sama da zai yi amfani da shi har bayan ya sauka daga mulki, amma marigayin ya ƙi karɓa saboda ba gwamnatin Najeriya za a ba wa ba.

“Sarkin Abu Dhabi ya tambayi shugaban ƙasa [Buhari] wane nau’in jirgi ya fi so. Sai [Buhari] ya ce idan gwamnatin Najeriya za a ba wa zan karɓa. Sai sarkin ya ce a’a naka ne na ƙashin kai, ta yadda ko da ka bar mulki za ka ci gaba da amfani da shi.

“Buhari ya ce ba ni buƙatar jirgi idan na bar mulki, ba zan ma iya kula da shi ba,” in ji Garba Shehu.

 

vanguard new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...

Sojoji sun kashe rikaken dan Bindiga Dan Dari Biyar a Sokoto

Dakarun Operation FANSAR YANMA sun yi nasarar fatattakar wani...

An kashe utane 30 a yakin Thailand da Cambodia

An shiga kwana na uku na faɗan kan iyaka...

Ba mu ƙayyade shekarun shiga ƙaramar sakandare JSS1 – Ma’aikatar Ilimi

Ma'aikatar Ilimi a Najeriya ta musanta rahoton da wasu...

Ido da Ido na ga yadda Sojojin Isra’ila ke kashe Falasdinawa – Tsohon Sojin Amurka

Wani tsohon sojan Amurk ya ce, ya ga yadda...

‘Yan majalisar Birtaniya 220 na neman ƙasar ta amice da ƙasar Falasɗinu

'Yan majalisar Birtaniya 220 sun nemi gwamnatin ƙasar ta...

Buhari yaki karbar kyautar Agogon lu’u-lu’u da jirgin sama – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Najeriya Muhammad Buhari,...

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...
X whatsapp