fidelitybank

Buhari ya yi ƙarin ladan tafiye-tafiye na DTA ga ma’aikatan gwamnati

Date:

 

 

 

Gwamnatin Taraiya ta amince da ƙarin kuɗin tafiye-tafiye da a ke baiwa maikata, wanda a turance a ke kira da Duty Tour Allocation, DTA.

Shugaban Hukumar kula da Albashi da Haƙƙoƙin Ma’aikata ta Ƙasa, Ekpo Nta ne ya baiyana hakan ga manema labarai a Abuja a jiya Alhamis.

Mata ya ce sabon ƙarin ladan tafiye-tafiyen zai fara aiki ne da ga 1 ga watan Fabrairu, inda ya baiyana farin ciki game da ci gaban da a ka samu.

“Wannan wani tagomashi ne ga ma’aikata. Gwamnatin Taraiya na ƙoƙarin kyautata walwalar ma’aikata.

“Ma’aikata da ke matakin albashi na 01 zuwa 01 yanzu za su riƙa karɓar N10,000, daga mataki na 05 zuwa 06 kuma N15,000, su kuma na mataki 07 zuwa 10 za su riƙa karɓar N17,500.

“Haka kuma masu matakin albashi na 12 zuwa 13 za su riƙa karɓar N20,000, na matakin 14 zuwa 15 kuma za su samu N25,000, inda mataki na 16 zuwa 17 za su riƙa karɓar N37,000,” in ji shi.

Nta ya tuna cewa, a baya, DTA ɗin ma’aikaci mai matakin albashi na 06 zuwa ƙasa N5,000 ne, yayin da na mataki 07 zuwa 14 N12,000 ne, sannan na matakin albashi 15 zuwa 17 N16,000 ne.

Ya yabawa Gwamnatin Taraiya da a kullum ta ke kula da walwalar ma’aikatan ta.

Shugaban ya kuma yabawa kafafen yaɗa labarai a bisa ƙoƙarin su na ilmantar da al’umma, inda ya hore su da su ɗore da kyawawan aiyukan da su ke yi

tribune news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp