Gwamnan jihar ONDO, Rotimi Akeredolu, ya dage cewa, dole ne gwamnan babban bankin Najeriya (CBN), Godwin Emefiele ya yi murabus, domin cimma burinsa na takarar shugaban kasa.
Akeredolu, Babban Lauyan Najeriya (SAN), ya ce, ya kamata Shugaba Muhammadu Buhari, ya tsige Emefiele daga mukamin Gwamnan CBN idan ya ki yin murabus.
Gwamnan na Ondo ya yi wannan kiran ne a wata sanarwa da ya wallafa a shafin sa na Facebook da aka tabbatar.
Matsin lambar na zuwa ne, tun bayan da wasu daga cikin masu riÆ™e da madafin iko a cikin gwamnatin Buhari suka ayyana sha’awarsa ta tsayawa takara a muÆ™amai. daban-daban. Wanda sabuwar dokar hukumar zaÉ“e mai zaman kanta ta Æ™asa ya nuna cewa, duk wani mai son tsayawa takara sai ya sauka daga muÆ™aminsa.