Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bi sahun shugabannin kasashen duniya wajen taya sabon zababben shugaban kasar Brazil Luiz Inacio Lula da Silva murnar lashe zaben da aka gudanar a kasar.
A wata sanarwa da babban mataimaki na musamman ga shugaban kasar kan kafofin yada labarai Malam Garba Shehu ya fitar, shugaba Buhari ya ce yana fatan sabon shugaban kasar zai karfafa alaka tsakanin kasashen biyu.
”Ina fatan yin aiki da sabon zababben shugaban kasar domin ci gaba da karfafa dankon zumuncin da alakar kasuwanci da ke tsakanin kasashenmu”, in ji sanarawa.
Lula ya yi nasara da karamin jinjaye kan abokin hammayarsa Jair Bolsonaro wanda har yanzu bai amince da shan kaye ba.