Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya mika sakon taya murna ga gwamna Aminu Bello Masari na jihar Katsina a yayin da yake murnar cika shekaru 72 da haihuwa.
Shugaban a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Malam Garba Shehu ya fitar a ranar Lahadin da ta gabata, ya ce “Ina yi maka fatan alheri da tsawon rai yayin da kake ci gaba da yi wa kasa hidima da sananniya na tawali’u da aiki tukuru”.
A cewar Shugaba Buhari: “Gwamna Masari, ya yi ayyuka da dama a kan ci gaban dimokuradiyyar matasanmu da kuma Katsina, inda ya kusa kawo karshen wa’adinsa biyu na Gwamna.
Ya yi nuni da cewa za a ci gaba da yabawa Masari kishin kasa, kwazonsa da kuma sanin yakamata a matsayin dukiyar kasa.