Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya isa garin Daura na jihar Katsina a yau Alhamis, a shirye-shiryen da za a yi na zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar tarayya da za a yi ranar Asabar.
A cewar wata sanarwa da Garba Shehu, babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa (Media & Publicity), ya fitar
Shugaban wanda ya samu tarba daga Gwamnan Jihar Katsina, Aminu Bello Masari da Darakta Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa (NIA), Amb. Ahmed Rufa’i Abubakar zai kada kuri’arsa ne a rumfar zabe da ke kusa da gidan sa a Daura, tare da matarsa Aisha Buhari da sauran ‘yan uwa.
Shugaban wanda jirginsa mai saukar ungulu ya sauka a Daura da karfe 5:25 na shirye-shiryen gudanar da zabe, ba wai a matsayin dan takara kamar yadda ya yi tun 2003 ba, sai a matsayin mai kada kuri’a.