Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya sauka a Abuja bayan kwana hudu da ya yi a birnin Addis Ababa, babban birnin Habasha.
Buhari ya halarci taron kungiyar tarayyar Afirka karo na 35.
A lokacin da ya ke Addis Ababa, Shugaba ya halarci taruka da dama tare da gudanar da tattaunawa, wadda ta hada ta ministar harkokin wajen Guinea Bissau Suzi Barbosa wadda ta yi wa shugaba na Najeriya bayani game da yunkurin juyin mulkn da aka yi a kasar.
Buhari ya sauka a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja da misalin karfe uku na rana.