fidelitybank

Buhari ya rusa haramtaccen kwamitin binciken kuɗi

Date:

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan wani ikirari da kwamiti na musamman da shugaban kasar ya kafa domin ya gudunar da bincike a kan cajin cirewa da ajiyar kudi a asusun banki.

Shugaban kwamitin, Gudaji Kazaure ya yi zargin cewa, wasu hukumomin da binciken ya shafa suna kokarin hana ruwa gudu game da aikin nasa, da kuma hana shi ya mika wa shugaba Muhammadu Buhari rahotonsa.

A cewar kwamitin wanda aka dora masa alhakin binciken cajin kudin ajiya da cire kudin tun daga shekara ta 2013 zuwa yanzu, ya gano cewa, babban bankin kasa ya tara fiye da naira tiriliyon tamanin, amma ya yi zargin cewa ana sama da fadi da kudin.

Malam Garba Shehu, shi ne mai magana da yawun shugaban kasa, ya yi karin bayanin kan wannan batun ga BBC.

“Wannan magana ta Gudaji Kazaure ba za a ce kwamiti ne ba. E, ya kafa kwamiti da kansa kuma ya nada jami’ai a ciki har da alkalin alkalan ƙasa da wasu mambobi. Ya sami shugaban kuma ya nuna masa kwato kudade na kasa za a yi.”

Garba Shehu ya ce, duk mutumin da ya gaya wa Buhari cewa zai kwato kudi, zai ce masa Allah-san-barka, sai dai ya musanta cewa shugaban kasa ne ya kafa kwamitin:

“A zahirin gaskiya, duk wanda ya san yadda gwamnati ke tafiya, babu yadda za a ce shugaban kasa a bangaren gwamnati ya kafa kwamiti ya ba wa dan majalisa sakatare, ya kuma kira alkalin alkalai ya nada shi mamba. Ai an yi wa tsarin mulki karen tsaye.

Ya ce kwamiti haramtacce ne, “ba shi da hurumi a doka, shi yasa Shugaba Muhammadu Buhari ya ce a rusa shi, a kuma kafa sabo wanda ke karkashin ministan shari’a.”

Ya kuma bayyana mamakinsa kan yawan kudaden da Gudaji Kazaure ke ambatowa a kalamansa da ke cewa biliyoyin daloli ne aka yi badakkalarsu.

“Wannan zargi na tiriliyan 160 da yake cewa sun salwanta, ina kudin suke? Tiriliyan 160 fa.”

Ya ce idan aka tattara dukiyar da dukkan bankunan Najeriya wuri guda, ba su kai kashi daya cikin uku na kudaden ba.

news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp