fidelitybank

Buhari ya rusa haramtaccen kwamitin binciken kuɗi

Date:

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan wani ikirari da kwamiti na musamman da shugaban kasar ya kafa domin ya gudunar da bincike a kan cajin cirewa da ajiyar kudi a asusun banki.

Shugaban kwamitin, Gudaji Kazaure ya yi zargin cewa, wasu hukumomin da binciken ya shafa suna kokarin hana ruwa gudu game da aikin nasa, da kuma hana shi ya mika wa shugaba Muhammadu Buhari rahotonsa.

A cewar kwamitin wanda aka dora masa alhakin binciken cajin kudin ajiya da cire kudin tun daga shekara ta 2013 zuwa yanzu, ya gano cewa, babban bankin kasa ya tara fiye da naira tiriliyon tamanin, amma ya yi zargin cewa ana sama da fadi da kudin.

Malam Garba Shehu, shi ne mai magana da yawun shugaban kasa, ya yi karin bayanin kan wannan batun ga BBC.

“Wannan magana ta Gudaji Kazaure ba za a ce kwamiti ne ba. E, ya kafa kwamiti da kansa kuma ya nada jami’ai a ciki har da alkalin alkalan ƙasa da wasu mambobi. Ya sami shugaban kuma ya nuna masa kwato kudade na kasa za a yi.”

Garba Shehu ya ce, duk mutumin da ya gaya wa Buhari cewa zai kwato kudi, zai ce masa Allah-san-barka, sai dai ya musanta cewa shugaban kasa ne ya kafa kwamitin:

“A zahirin gaskiya, duk wanda ya san yadda gwamnati ke tafiya, babu yadda za a ce shugaban kasa a bangaren gwamnati ya kafa kwamiti ya ba wa dan majalisa sakatare, ya kuma kira alkalin alkalai ya nada shi mamba. Ai an yi wa tsarin mulki karen tsaye.

Ya ce kwamiti haramtacce ne, “ba shi da hurumi a doka, shi yasa Shugaba Muhammadu Buhari ya ce a rusa shi, a kuma kafa sabo wanda ke karkashin ministan shari’a.”

Ya kuma bayyana mamakinsa kan yawan kudaden da Gudaji Kazaure ke ambatowa a kalamansa da ke cewa biliyoyin daloli ne aka yi badakkalarsu.

“Wannan zargi na tiriliyan 160 da yake cewa sun salwanta, ina kudin suke? Tiriliyan 160 fa.”

Ya ce idan aka tattara dukiyar da dukkan bankunan Najeriya wuri guda, ba su kai kashi daya cikin uku na kudaden ba.

nigerianewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp