Shugaban Muhammadu Buhari, ya rantsar da kwamitin miƙa mulki, wadda za ta gudanar da shirye-shiryen miƙa mulki zuwa wata sabuwar gwamnatin da za a zaɓa cikin wannan wata.
Shugaban wanda ya samu wakilcin sakataren gwamnatin tarayya Boss Mustapha, ya ce dole a adana ci gaban da gwamnatinsa ta samar.
A makon da ya gabata ne shugaban shugaban ƙasar ya amince da kafa kwamitin tare da sanya hannu kan dokar ta ta samar da kwamitin, domin halasta ayyukansa.
Yayin da yake rantsar da mambobin kwamitin Boss Mustapha ya ce wannan wani abu ne na tarihi da gwamnatinsu ta samar wajen nuna yadda ta damu wajen bunƙasa harkokin dimokradiyya a ƙasar.
A ranar 25 ga watan Fabrairun da muke ciki ne dai ‘yan ƙasar za su zaɓi sabon shugaban ƙasar na gaba, da zai gaji kujerar shugaba Buhari.
Inda kuma za a miƙa mulki ga sabuwar gwamnatin ranar 29 ga watan Mayun shekarar da muke ciki.