Festus Keyamo, Karamin Ministan Kwadago da Aiki, ya ce gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta rage karfin Boko Haram zuwa “kusan babu komai.”
Keyamo, wanda ya yi ikirarin cewa gwamnatin Buhari ta gaji matsalar Boko Haram, ya kuma yarda cewa ba a kawar da ‘yan ta’addan gaba daya ba.
Kakakin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin wata tattaunawa da yayi da gidan talabijin na Trust.
Ya ce, “Me muka gada? Mun gaji matsalar Boko Haram. A lokacin sun kwace kananan hukumomi sama da goma sha hudu a yankin arewa maso gabas tare da kafa tutocinsu. Mun gaji rikicin manoma da makiyaya da ke faruwa tun kafin zamanin Obasanjo (Olusegun). Waɗannan matsaloli ne na wanzuwa.