fidelitybank

Buhari ya nada Dr. Doyin Salami a matsayin mashawarci

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada Dr. Doyin Salami, a matsayin babban mai ba shi shawara kan harkokin tattalin arziki.

Salami, mai shekaru 59, ya kasance shugaban kwamitin ba da shawara kan tattalin arziki na shugaban kasa (PEAC).

Salami ya kammala karatun digiri na uku a shekarar 1989 a fannin tattalin arziki a Kwalejin Queen Mary, a Jami’ar London, Doyin Salami, wanda manajan darakta ne kuma shugaban kasuwancin a KAINOS Edge Consulting Limited.

Ya kasance memba na Adjunct Faculty a makarantar kasuwanci ta jihar Legas, (LBS), Pan-Atlantic, inda kwanan nan ya sami matsayi Senior Fellow/ Associate Professor.

A na sa ran babban mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tattalin arziki zai yi jawabi a kan dukkan batutuwan da su ka shafi tattalin arzikin cikin gida tare da gabatar da ra’ayoyi a kansu ga shugaban kasa.

Har ila yau, zai sa ido sosai kan abubuwan da ke faruwa a cikin ƙasa da na duniya, abubuwan da ke faruwa tare da samar da martanin manufofin da suka dace.

A cewar wata sanarwa da mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai, Femi Adesina ya fitar, Salami zai bunkasa tare da ba wa shugaban kasa shawara kan manufofin tattalin arzikin kasa, domin samar da kwanciyar hankali a fannin tattalin arziki, inganta ci gaba, samar da ayyukan yi, da kawar da talauci da dai sauransu.

A halin yanzu, Buhari ya na da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin tattalin arziki, Adeyemi Dipeolu wanda ke aiki a ofishin mataimakin shugaban kasa. An nada Dipeolu a shekarar 2015.

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp