fidelitybank

Buhari ya nada Dr. Doyin Salami a matsayin mashawarci

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada Dr. Doyin Salami, a matsayin babban mai ba shi shawara kan harkokin tattalin arziki.

Salami, mai shekaru 59, ya kasance shugaban kwamitin ba da shawara kan tattalin arziki na shugaban kasa (PEAC).

Salami ya kammala karatun digiri na uku a shekarar 1989 a fannin tattalin arziki a Kwalejin Queen Mary, a Jami’ar London, Doyin Salami, wanda manajan darakta ne kuma shugaban kasuwancin a KAINOS Edge Consulting Limited.

Ya kasance memba na Adjunct Faculty a makarantar kasuwanci ta jihar Legas, (LBS), Pan-Atlantic, inda kwanan nan ya sami matsayi Senior Fellow/ Associate Professor.

A na sa ran babban mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tattalin arziki zai yi jawabi a kan dukkan batutuwan da su ka shafi tattalin arzikin cikin gida tare da gabatar da ra’ayoyi a kansu ga shugaban kasa.

Har ila yau, zai sa ido sosai kan abubuwan da ke faruwa a cikin ƙasa da na duniya, abubuwan da ke faruwa tare da samar da martanin manufofin da suka dace.

A cewar wata sanarwa da mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai, Femi Adesina ya fitar, Salami zai bunkasa tare da ba wa shugaban kasa shawara kan manufofin tattalin arzikin kasa, domin samar da kwanciyar hankali a fannin tattalin arziki, inganta ci gaba, samar da ayyukan yi, da kawar da talauci da dai sauransu.

A halin yanzu, Buhari ya na da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin tattalin arziki, Adeyemi Dipeolu wanda ke aiki a ofishin mataimakin shugaban kasa. An nada Dipeolu a shekarar 2015.

guardian newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Har yanzu ina LP kuma ni ne zan iya saita Najeriya – Datti

Datti Baba-Ahmed, tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa a...

APC ta zama buhun kusa ta gaza a Najeriya – Amaechi

Tsohon gwamnan jihar Ribas, Chibuike Amaechi ya bayyana jam'iyyar...

An fara samun takun saka tsakanin Turkiyya da Najeriya a kan kungiyar Gulen

Kungiyar kare hakkin musulmi, MURIC, ta bukaci shugaban kasar...

ArziÆ™in Najeriya ya Æ™aru da kashi 3.13 a farkon 2025 – NBS

Tattalin arzikin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 cikin...

Kamfanonin lantarki za su katse wutar lantarki saboda bashi

Kamfanonin samar da wutar lantarki, sun ce suna iya...

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

ÆŠan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai Æ™arfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...
X whatsapp