Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da nadin Ahmed Halilu a matsayin Manajan Darakta na Kamfanin Buga da Ma’adanai na Najeriya NSPMC Plc.
An ce Halilu kane ne ga uwargidan shugaban kasa, A’isha Buhari, kuma ya jagoranci kamfanin ne a matsayin riko bayan murabus din Abbas Masanawa a ranar 16 ga watan Mayu.
Rahotanni sun ce shugaban ya amince da nadin ne biyo bayan shawarar da gwamnan babban bankin Najeriya, Godwin Emefiele, wanda ke rike da mukamin shugaban hukumar NSPMC ya bayar.
Halilu ya halarci babban kwas na 39, 2017 na National Institute for Policy and Strategic Studies Kuru, Jos, wanda ya kai ga lambar yabo ta Memba na Cibiyar National Institute, mni.
Ya yi digirin farko a fannin Noma B. (Agric), Masters in Business Administration, da Masters in International Affairs and Diplomacy, duk a Jami’ar Ahmadu Bello Zariya.
Har ila yau, ya bayyana cewa yana da gogewar sama da shekaru 23 a harkar banki, inda ya yi aiki da bankin kasa da kasa na African International Bank Limited, AIB, da Zenith Bank Plc, kuma mamba ne a Cibiyar Gudanarwa ta Najeriya, NIM.,