fidelitybank

Buhari ya na da ‘yancin tsayar da dan takarar sa a zaben shugaban jam’iyya – Fayemi

Date:

Gwamnan jihar Ekiti, Kayode Fayemi, a ranar Alhamis, ya ce, ba shi da masaniyar wani shafaffu ko wanda ake so shugaba Muhammadu Buhari zai tsaya takarar shugaban kasa gabanin babban taron jam’iyyar APC mai zuwa a gobe Asabar.

Gwamnan, ya ce, duk da cewa shugaban kasa na da hakkin ya samu wanda zai fi so, shi Buhari zai bukaci ya yi wa irin wannan kamfen a yayin babban taron.

“Game da tambayarki akan ko shugaban kasa ya nada wani ya zama shugaban jam’iyyar, ba ni da masaniya akan hakan,” in ji shi.

Ya kuma ce “Shugaban kasa yana da ‘yancin samun wanda ya dace amma a jam’iyyarmu, bari shi (Buhari) ya zo ya yi wa waccan takara yakin a dandalin Eagle Square ranar Asabar. Idan dan takararsa ya yi nasara, to, idan dan takararsa ya yi rashin nasara, to zai ci gaba da rayuwa da hakan.

Mista Fayemi ya bayyana haka ne a wani taron da cibiyar dimokuradiyya da ci gaban Afirka ta Yamma (CDD) ta shirya a Abuja a lokacin da yake amsa tambaya daga wakilin AIT.

A gobe Asabar ne jam’iyyar APC mai mulki za ta gudanar da babban taronta na kasa a dandalin Eagles Square da ke Abuja, inda wakilai kusan 4,000 daga jihohin kasar nan 36 da kuma babban birnin tarayya Abuja za su halarta.

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miĈ™a saĈ™on ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe Ĉ´an ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin Ĉ´an Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ĉ˜arfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barĈ™wanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama Ĉ´an Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na Ĉ™asa – Fadar Shugaban Ĉ˜asa

Fadar shugaban Ĉ™asa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan ĈŠalibai Mata a Kano

Babbar Kotun ShariÊĵar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban Ĉ™asa, Mohammed Namadi Sambo, ya Ĉ™aryata...
X whatsapp