Shugaba Muhammadu Buhari, ya miƙa sakon ta’aziyyarsa ga iyalan shugaban ƙungiyar al’umar Ibo ta Ohaneze kan mutuwar jagoran ƙungiyar Farfesa George Obiozor.
A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar Femi Adesina ya fitar, shugaba Buhari ya ce ya ‘kaɗu matuƙa’ da jin labarin rasuwar mista Obiozor.
Shugaban ya kuma jajanta wa iyalan marigayin da gwamnati da al’umar jihar Imo tare da ƙungiyar da kuma al’umar Ibo ‘yan Najeriya da mazauna ƙasashen ƙetare.
Buhari ya bayyana mutuwar jagoran ƙungiyar ta Ohaneze da cewa babban rashi ne ga ƙasar, yana mai cewa ƙasar ba za ta taɓa manta irin gudunmowar da ya bai wa ƙasar ba.
Mista Obiozor dai ya taɓa riƙe muƙaman jakadan Najeriya a ƙasashen Amurka da Cyprus da Isr’ila da kuma muƙamin babban darakta a cibiyar kula da al’amuran ƙasashen waje ta Najeriya (NIIA).