fidelitybank

Buhari ya mayar da jami’ar kimiyyar lafiya zuwa ta likitanci ta tarayya

Date:

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari,ya bada tabbacin gwamnatin tarayya za ta karbe jami’ar kimiyar lafiya ta Uburu, Ebonyi tare da sarrafa ta a matsayin jami’ar likitanci ta tarayya.

Shugaban ya bayyana hakan ne a wajen wani liyafar cin abincin dare da aka yi masa a ranar Alhamis a Abakaliki, bisa bukatar farko da gwamna David Umahi na Ebonyi ya gabatar.

Jami’ar dai tana karamar hukumar Ohaozara ne a jihar.

Shugaban ya shaida wa al’ummar Ebonyi cewa, an fara aiwatar da shirin sauya mallakar jami’ar kuma ‘’ za a kammala shi nan ba da jimawa ba.

A kan bukatar da gwamnan jihar ya yi na sayen kayan aikin filin jirgin da kudinsu ya kai Naira biliyan 10, shugaban ya yi alkawarin gano matsayin ma’aikatar sufurin jiragen sama dangane da hakan.

Ya kuma bayyana kwarin gwiwar cewa, wadannan cibiyoyi da ma sauran su za su kara kaimi wajen bunkasar tattalin arzikin jihar musamman ma kasa baki daya.

Buhari wanda ya baiwa gwamnati da al’ummar Ebonyi tabbacin goyon bayan gwamnatinsa, domin baiwa gwamnan damar cimma burinsa na jihar, ya gode musu bisa tarbar da aka yi masa a ziyarar kwanaki biyu da ya kai jihar.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp