fidelitybank

Buhari ya mayar da jami’ar kimiyyar lafiya zuwa ta likitanci ta tarayya

Date:

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari,ya bada tabbacin gwamnatin tarayya za ta karbe jami’ar kimiyar lafiya ta Uburu, Ebonyi tare da sarrafa ta a matsayin jami’ar likitanci ta tarayya.

Shugaban ya bayyana hakan ne a wajen wani liyafar cin abincin dare da aka yi masa a ranar Alhamis a Abakaliki, bisa bukatar farko da gwamna David Umahi na Ebonyi ya gabatar.

Jami’ar dai tana karamar hukumar Ohaozara ne a jihar.

Shugaban ya shaida wa al’ummar Ebonyi cewa, an fara aiwatar da shirin sauya mallakar jami’ar kuma ‘’ za a kammala shi nan ba da jimawa ba.

A kan bukatar da gwamnan jihar ya yi na sayen kayan aikin filin jirgin da kudinsu ya kai Naira biliyan 10, shugaban ya yi alkawarin gano matsayin ma’aikatar sufurin jiragen sama dangane da hakan.

Ya kuma bayyana kwarin gwiwar cewa, wadannan cibiyoyi da ma sauran su za su kara kaimi wajen bunkasar tattalin arzikin jihar musamman ma kasa baki daya.

Buhari wanda ya baiwa gwamnati da al’ummar Ebonyi tabbacin goyon bayan gwamnatinsa, domin baiwa gwamnan damar cimma burinsa na jihar, ya gode musu bisa tarbar da aka yi masa a ziyarar kwanaki biyu da ya kai jihar.

vanguard newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

INEC za ta fitar da sabbin ƙa’idojin duba sakamakon zaɓe

A shirye-shiryen da take yi gabanin babban zaɓen Najeriya...

Isra’ila ta amince da sharuɗɗan yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce Isra'ila ta amince...

Buhari ba zai taɓa cin amanar Tinubu ba – Garba Shehu

Tsohon babban mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai...

Mutane 207 ne suka mutu a ambaliyar Neja – NSEMA

Darakta Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta...

Jiga-jigan jam’iyyar PDP za su sauya sheƙa don tunkarar APC a 2027

Wasu jiga-jigan jam'iyyar PDP da suka hada da tsohon...

Za a ƙaddamar da jam’iyyar hammaya da za ta tunkari APC

Gamayyar jam'iyyun adawa a ranar Talata, ta amince da...

Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram Takwas a jihar Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta sun kashe aƙalla...

Sauya sunan Kwaleji a Oyo ya fusata Dalibai

Ɗaliban kwalejin fasaha ta Ibadan sun gudanar da zanga-zanga...

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Dantata

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta'aziyya...

Trump ba shi da hankali ko tunani a kan harajin sa – Elon Musk

Tsohon mai ba shugaban Amurka Donald Trump shawara kan...

Dangote ya rage man fetur lita 840

Matatar man Dangote ta rage farashin litar man fetur...
X whatsapp