Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya koma fadar gwamnatinsa da ke Abuja, bayan shafe kwanaki a mahaifarsa ta Daura ta jihar Katsina.
A wani saƙo da mai magana da yawun shugaban Malam Garba Shehu ya wallafa a shafinsa ta Twitter, ya ce shugaban ya koma Abuja ne bayan kwanaki 18.
Karanta Wannan: Matasa ku yi koyi da Osinbajo – Buhari
Saƙon ya ƙara da cewa shugaban ya yi amfani da lokacin wajen gudanar da zaɓen shugaban ƙasa tare da ziyara da ya kai Maiduguri da taron Majalisar Dinkin Duniya da ya halarta a birnin Doha na ƙasar Qatar.
Malam Garba Shehu ya ƙara da cewa nan gaba kaɗan ne cikin wannan makon shugaban tare da sauran ma’aikatan fadarsa da suka yi rajistar zaɓe a Daura za su sake komawa domin halartar zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisun dokokin jihohi.