Shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya yi watsi da shirin gwamnonin APC biyu na ya ɗauki wani ɗan takara a matsayin shugaban jam’iyya na gaba, gabanin babban taron ta na kasa.
The Nation ta rawaito cewa, Buhari ya bukaci gwamnonin biyu, su kai shawarinsu gaban kwamitin rikon kwarya, takwarorinsu gwamnoni, da masu ruwa da tsaki, domin duba yuwar hakan.
Gwamnonin sun garzaya ga Buhari ne, domin ya goyi bayan ɗan takarar da suke so ya zama shugaban APC, lamari dai bai yiwa sauran gwamnoni daɗi ba.