fidelitybank

Buhari ya kashe Ilimi zamu yi jana’izarta – NANS

Date:

Kungiyar dalibai ta kasa NANS, ta shiyyar Kudu-maso-Yamma, ta zargi shugaban kasa Mohammed Buhari da binne ilimin al’umma a kasar, inda ta ce a shirye take ta gudanar da jana’izar ta.

Hakan ya fito ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kodinetan NANS kuma mai magana da yawun hukumar, Adegboye Olatunji da Awoyinfa Opeoluwa, bi da bi, a ranar Litinin.

Kungiyar daliban ta ce za su sake buga titina a cikin kwanaki masu zuwa.

Wani bangare na sanarwar ya kara da cewa: “Ya dace mu ja hankalin jama’a da sauran kasashen duniya game da cin mutuncin daliban Najeriya da gwamnatin Buhari ta yi.

“Muna son daliban Najeriya su kasance a shirye don daukar gagarumin mataki kan yajin aikin ASUU. Mu a fili muke cewa wannan gwamnati ta sabawa ilimin al’umma kuma hakan ya saba wa muradin miliyoyin dalibai da matasa.

“A kwanaki masu zuwa, za mu mamaye titunan yankin Kudu maso Yamma domin gudanar da bikin jana’izar ilimin al’umma na karshe a kasar nan saboda abin da gwamnatin Buhari ke wakilta ke nan,” in ji sanarwar.

thisdaynews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp