Kungiyar dalibai ta kasa NANS, ta shiyyar Kudu-maso-Yamma, ta zargi shugaban kasa Mohammed Buhari da binne ilimin al’umma a kasar, inda ta ce a shirye take ta gudanar da jana’izar ta.
Hakan ya fito ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kodinetan NANS kuma mai magana da yawun hukumar, Adegboye Olatunji da Awoyinfa Opeoluwa, bi da bi, a ranar Litinin.
Kungiyar daliban ta ce za su sake buga titina a cikin kwanaki masu zuwa.
Wani bangare na sanarwar ya kara da cewa: “Ya dace mu ja hankalin jama’a da sauran kasashen duniya game da cin mutuncin daliban Najeriya da gwamnatin Buhari ta yi.
“Muna son daliban Najeriya su kasance a shirye don daukar gagarumin mataki kan yajin aikin ASUU. Mu a fili muke cewa wannan gwamnati ta sabawa ilimin al’umma kuma hakan ya saba wa muradin miliyoyin dalibai da matasa.
“A kwanaki masu zuwa, za mu mamaye titunan yankin Kudu maso Yamma domin gudanar da bikin jana’izar ilimin al’umma na karshe a kasar nan saboda abin da gwamnatin Buhari ke wakilta ke nan,” in ji sanarwar.