Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya karbi bakuncin takwaransa na kasar Ghana, Nana Akufo-Addo a fadar shugaban kasa da ke Abuja.
Buhari ya tarbi shugaban na kasar Ghana ne jim kadan bayan gama ganawarsa da gwamnonin jamâiyyar All Progressives Congress (APC), a ranar Talata, 22 ga watan Fabrairu.
Labarin ganawar shugabannin na kasashen Afrika biyu na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara a kafofin sadarwa ta zamani, Buhari Sallau ya fitar a shafinsa na Twitter.
Sai dai babu wani cikakken bayani game da abun da shugabannin za su tattauna a kai a daidai lokacin kawo wannan bayanin.