Shugaba Buhari ya karbi bakuncin kwamitin zartarwa na kungiyar masu samar da takin zamani ta ƙasa, ya na mai cewa, jagoranci ya dora Najeriya a kan turbar da ta dace a matsayin kasar da ke kan gaba wajen samar da taki a Afirka.
Buhari ya bayyana hakan ne a ranar Talata a gidan gwamnati da ke Abuja, yayin da ya karbi bakuncin kwamitin zartarwa na kungiyar masu samar da takin zamani ta Najeriya.
A nasa jawabin, shugaban ya bayyana cewa, wannan gagarumin nasara da aka samu, cikin kankanin lokaci, ya tabbatar da ci gaba da zuba jari a fannin daga kamfanoni masu zaman kansu, inda ya bude hanyar samun riba mai kyau ga miliyoyin ‘yan Najeriya da masu zuba jari na kasashen waje.
Ya ce, “Tare da kamfanonin hada-hadar hannayen jarin mu sama da saba’in ke aiki, Najeriya na kan hanyarta ta zama cibiyar samar da takin zamani a Afirka. Kuma tare da manyan wuraren samar da Urea, tabbas Najeriya ta zama abun kwatance a duniya a samar da takin Urea.”