Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a ranar Juma’a ya dawo Abuja daga Landan bayan ya duba lafiyarsa.
Shugaba Buhari ya bar Abuja, domin duba lafiyarsa na yau da kullun a Landan a ranar 6 ga Maris.
Tun da farko dai shugaban ya so ya fara ziyarar jinya ne daga birnin Nairobi na kasar Kenya, bayan ya halarci shirin kula da muhalli na Majalisar Dinkin Duniya (UNEP) na shekaru 50 a kasar, a ranar 5 ga Maris, amma ya dawo Najeriya a ranar 4 ga Maris.
Mai magana da yawun shugaban Femi Adesina, a ranar 1 ga Maris, a cikin wata sanarwa ya ce, daga Kenya, shugaban zai wuce Landan, domin duba lafiyarsa na yau da kullun wanda zai dauki akalla makonni biyu.
Sai dai shugaban ya koma Abuja kafin ya tafi Landan ranar 6 ga watan Maris.