Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya amince da kafa sabuwar hukumar gwamnati mai suna ‘Nigeria Data Protection Bureau’ (NDPB) mai kare bayanai da sirrin kasa a zamance.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa, an kafa hukumar ne bayan Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani, Farfesa Isa Ali Pantami ya bukaci a kafa ta.
A cikin wata sanarwa da aka fitar a madadin Pantami, Uwa Suleiman, hadiminsa a bangaren yada labarai ta ce, an kafa NDPB ne bisa tsari mafi kyau kuma zai mayar da hankali ne, domin kare bayanai da sirrin kasa da wasu ayyukan.
Ya ce, bayan samun nasarar aiwatar da tsarin zamantar da tattalin arzikin Najeriya na ‘National Digital Economy Policy and Strategy’ (NDEPS), hukumomi da dama sun zamantar da ayyukansu,