Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar da rukunin gidaje 76 da suka hada da titunan cikin gida da magudanun ruwa da rijiyar burtsatse ta tsakiya da tankunan ruwa da wutar lantarki a Gama-Gwari daura da titin Jaba Fanisau a karamar hukumar Fagge a jihar Kano.
Gidan ya ƙunshi gine-gine 48 mai dakuna 2, da gine-gine 24 mai dakuna 3 da sai mai dakuna 1.
An bayar da kwangilar ne a watan Mayun 2017 a kan jimillar Naira miliyan 608.8. Kammala aikin titin, magudanan ruwa da kwalta an kashe Naira miliyan 438.2, samar da wutar lantarki da na’urar taransfoma 500kva ya kai Naira miliyan 82.2, yayin da rijiyar burtsatse mai motsi ta kai Naira miliyan 88.3.
Gwamnatin Jihar Kano ce, ta samar da filayen da za ayi aikin.
Shugaba Buhari wanda ya samu wakilcin Ministan Tsaro, Manjo Janar Bashir Salihi Magashi, ya ce, gidajen misali ne na cika alkawarin kawo sauyi da jam’iyyar APC ta yi a lokacin da ta nemi izini daga ‘yan Najeriya don kafa gwamnati a 2015.
“Wannan misali ne mai kyau na wasu damar ci gaba da hadin gwiwar gwamnatocin za su iya samarwa, kuma ina da kwarin gwiwar cewa, idan aka samar da karin filayen, gwamnatin tarayya za ta iya yin fiye da haka.”