Shugaba Muhammadu Buhari, ya ƙaddamar da aikin haƙo man fetur a yankin Kolmani da ke tsakanin jihohin Bauchi da Gombe.
Lokacin ƙaddamarwar shugaba Buhari ya umurci kamfanin mai NNPCL ya yi duk mai yiwuwa a hurumin da doka ta ba shi, domin tabbatar da sun janyo masu zuba jari domin bunƙasa sarrafa man fetur a Arewacin Najeriya.
Haka kuma Shugaba Buhari ya ce ya tattauna da gwamnonin Bauchi da Gombe, inda suka tabbatar masa da za su bayar da haɗin kai domin ci gaba da aikin bunƙasa haƙo man fetur ɗin.
Bayan Shugaba Muhammadu Buhari ya yi wannan ƙaddamarwa, BBC ta tattauna da ɗaya daga cikin manyan jami’an kamfanin mai na NNPC da ke kula da inda kamfanin ke zuba jari, Bala Wunti, inda ya shaida wa BBC cewa an gano aƙalla ganga fiye da biliyan ɗaya ta ɗanyen man fetur a ƙarƙashin ƙasa.
Kazalika ya ce ana fatan gina matatar mai da kamfanonin samar da taki da kuma iskar gas.
Matatar man da ake fatan ginawa za ta riƙa sarrafa ganga fiye da 100,000 a kullum.