Wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya ya nuna cewa, Najeriya ce a kan gaba, wajen yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a faɗin Najeriya, wanda adadin yara miliyan 13 da ke zaune a gida, ko suke gararamba a gari.
Bayan waɗannan alƙaluma na MDD tuni gwamnatin tarayya ta ce, ta fara wani bincike, domin kididdige yawan yaran da ba sa zuwa makaranta.
A cewar shugaban shirin tallafa wa masu karamin karfi na kasa, wato National Social Investment Programme da ma’aikatar ayyukan jin kai ke gundanarwa, kawo yanzu an gudanar da aikin kidayar yaran a wasu jihohi.
Dr. Umar Buba Bindir, ya shaida wa BBC cewa, shugaba Muhammadu Buhari ya kadu sosai a lokacin da ya ji alkaluman da aka fitar na yaran da sa zuwa makaranta a Najeriya