fidelitybank

Buhari ya jajanta wa Jonathan

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jajantawa tsohon shugaban kasa Goodluck Ebele Jonathan bisa rasuwar ma’aikatan sa guda biyu a wani hatsarin mota da ya rutsa da su.

Shugaban kasar, a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a ta hannun mai magana da yawunsa, Garba Shehu, ya bi sahun ‘yan kasar wajen addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu.

Shugaba Buhari ya bukaci iyalansu da su kalli rasuwarsu a matsayin sadaukarwa ga kasa.

Shugaban wanda ya nuna godiya ga Allah Madaukakin Sarki da ya sa Shugaba Jonathan ya tsira daga hatsarin, ya bukace shi da kada ya shagaltu da tafiye-tafiyen da yake yi a cikin gida da waje da ya shafi samar da zaman lafiya a gida da waje.

Aminiya ta ruwaito yadda ayarin motocin Jonathan suka yi hatsari a kusa da filin jirgin saman Nnamdi Azikwe, Abuja.

Da yake mayar da martani kan lamarin, shugaban kungiyar matasan kabilar Ijaw na kasa, Peter Timothy Igbifa, ya yi zargin cewa, hatsarin wani shiri ne da wasu makarkashiya suka shirya don kawo karshen rayuwar tsohon shugaban kasar gabanin babban zabe na 2023.

A cewarsa, ‘yan sandan sun yi amfani da kansu ne a matsayin garkuwar dan Adam wajen kare Jonathan kuma a cikin haka ne suka biya farashi mai tsoka.
Ya yi barazanar cewa, matasan Neja-Delta za su durkusar da tattalin arzikin kasar idan wani sharri ya samu Jonathan.

Sai dai hukumar kiyaye haddura ta kasa (FRSC) ta shaida wa Aminiya cewa “gudu” ne zai iya haddasa hadarin.

Kwamandan hukumar dake kula da reshen babban birnin tarayya Abuja, Samuel Ogar Ochi, ya ce an fara gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

vanguard news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp