fidelitybank

Buhari ya jagoranci taron majalisar tsaro

Date:

Shugaba Muhammadu Buhari, ya jagoranci taron majalisar tsaro ta ƙasa a Abuja a yau Laraba.

An tattauna kan batutuwa da dama musamman ma kan tsari na tsaro da hukumomin tsaro suka yi gabanin babban zaɓen ƙasar da ke tafe.

A lokacin da yake tattaunawa manema labarai bayan taron, sufeton ‘yan sanda, Usman Alkali Baba, ya ce sun shirya tsaf domin gudanar da zaɓen da ke tafe.

Ya ce sun tanadi matakan tsaro da dama domin ƙare lafiyar waɗanda za su kaɗa kuri’a, inda ya buƙace su da su fito ba tare wata fargaba ba domin zaɓar wanda suke so.

Ya ce sun kuma faɗa wa shugaban ƙasa cewa yanayin tsaro na kyautata a Najeriya.

Shi ma da yake magana bayan kammala taron majalisar tsaron, ministan shari’a kuma babban attoni janar na ƙasa, Abubakar Malami, ya ce abin da ya sa gwamnatin tarayya ta kira wannan taro shi ne domin ji daga hafsoshin tsaron ƙasar da shugabannin sauran hukumomin tsaro kan irin shirin da suka yi gabanin zaɓe da ke tafe.

Ya ce bayan ji daga garesu, gwamnati ta yi na’am da irin shirye-shiryensu, inda ya ce gwamnatin ta tanadi duk abin da ya kamata wajen ganin a samu nasarar gudanar da zaɓukan lami lafiya.

Manyan jami’an gwamnati da dama ne suka halarci taron.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp