fidelitybank

Buhari ya hana a cike guraben ma’aikata sama da dubu dari – Sani Bala Tsanyawa

Date:

Wani dan Majalisar dokokin tarayya, Sani Bala Tsanyawa, ya ce, akwai guraben aikin gwamnatin tarayya sama da dubu ɗari da ashirin amma shugaban kasar Muhammadu Buhari ya hana a cike su.

Honorabul Sani Bala Tsanyawa, wanda shi ne shugaban Kwamitin kula da Ayyukan gwamnati na Majalisar Wakilan Najeriya ne ya tabbatar da hakan a hirarsa da BBC Hausa.

Ya ce tun a shekarar 2019 ne Shugaba Buhari ya sanar wa majalisar dokoki ɗaukar matakin a lokacin da ya je zaurenta domin gabatar da kasafin kuɗi.

A cewarsa “Lokacin gabatar da kasafin kuɗi da (shugaban kasa) ya kawo wa majalisa, yake faɗa cewa ya dakatar da ɗaukan aiki a ‘mainstream civil service’ – wato ma’aikatan da ke a aiki a ma’aikatu na kwaryar aikin gwamnati.”

Ya ce tun da shugaban ƙasar ya sanya wannan haramci ba a ƙara ɗaukar aiki ba a irin waɗannan ma’aikatu.

Sai dai a cewarsa an bai wa wasu ma’aikatun gwamnatin damar daukar ma’aikata saboda dalilai masu ƙarfi.

Bangarorin da aka yi wa rangwamen sun haɗa da na tsaro da lafiya – sakamakon barkewar annobar korona.

Ya kara da cewa “Daga shekara biyar a baya zuwa yau, bincikenmu ya nuna cewa ma’aikata dubu ɗari da talatin ne suka bar aiki.”

“Wasun su ko dai sun mutu, wasu kuma sun yi ritaya, wasu kuma sun samu wani aikin na daban sun bar na gwamnatin tarayya.”

Ya ce amma a tsawon waɗannan shekaru biyar bayan sanya haramcin, mutum dubu shidda da dari bakwai ne kacal gwamnatin tarayya ta ɗauka aiki. In ji BBC.

Sannan ya ce duk da haka har yanzu yawan guraben na kara yawa saboda a kodayaushe akan samu ma’aikatan da ke mutuwa ko ajiye aiki, to amma har yanzu ba a cire wannan haramci ba.

Sai dai ya ce, akwai wasu hukumomin da a wani lokaci sukan dauki ma’aikata, kamar babban bankin Najeriya (CBN) da hukumar sadarwa ta kasa (NCC), amma ba a ma’aikatun kwaryar aikin gwamnati ba, waɗanda a turance ake kira ‘ministries’.

vgn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...

Wike ya caccaki Rotimi a kan jam’iyyar ADC

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya caccaki tsohon...

Tsige ni daga mukamin Wazirin Gaya ba a kan doka ba ne – Usman Alhaji

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya...

Gini mai bene uku ya danne Mutane a jihar Legas

Wani gini mai bene uku ya rufta a unguwar...

Kotu ta daure Matashi dan Tiktok da ya ke sanya rigar mama

Wata kotu a jihar Kano, ta yanke wa wani...

Peter Obi ka gaggauta ficewa daga jam’iyyar mu nan da awa 48 – Labour Party

Bangaren jam’iyyar Labour da Julius Abure ke jagoranta, ya...
X whatsapp