fidelitybank

Buhari ya halarci bikin tunawa da ‘yan Mazan jiya

Date:

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya halarci bikin taron tunawa da ‘yan mazan jiya, wanda kuma shi ne na ƙarshe da shugaban ƙasar zai halarta a matsayinsa na shugaban ƙasa kuma babban kwamandan rundunonin tsaro na ƙasar.

A wata sanarwa da mataimaki na musamman ga shugaban kan kafofin sadarwa na zamani Bashir Ahmad ya wallafa a shafinsa na Tuwita ya ce wannan ne karo na takwas kuma na ƙarshe da Buhari ke halartar wannan biki a matsayinsa na shugaban ƙasa.

Daga cikin waɗanda suka halarci bikin wanda aka gudanar a Abuja babban birnin ƙasar sun haɗar da mataimakin shugaban ƙasar Farfesa Yemi Osinbajo da shugaban majalisar dattawan ƙasar Sanata Ahmad Lawan da kakakin majalisar wakilai Femi Gbajabiamila da babban alƙalin alƙalan ƙasar, Mai shari’a Olukayode Ariwoola, da sauran manyan jami’an gwamnati.

Ana dai gudanar da wannan biki ne a duk shekara domin tunawa da irin gagarumar gudunmowar da tsoffin dakarun ƙasar suka bayar wajen zaman lafiya da ci gaban ƙasar.

A wajen bikin Shugaban ƙasar da sauran jami’an gwamnati kan ajiye furanni domin nuna jinjina ga ‘yan mazan jiyan, tare da yin faretin girmama wa ga shugaban ƙasa, sannan kuma shugaban ya saki fararen tattabaru suka tashi sama duk domin nuna tunawa da irin ƙwazon da ‘yan mazan jiyan suna nuna ga ƙasar.

vanguard newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp