Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya halarci bikin taron tunawa da ‘yan mazan jiya, wanda kuma shi ne na ƙarshe da shugaban ƙasar zai halarta a matsayinsa na shugaban ƙasa kuma babban kwamandan rundunonin tsaro na ƙasar.
A wata sanarwa da mataimaki na musamman ga shugaban kan kafofin sadarwa na zamani Bashir Ahmad ya wallafa a shafinsa na Tuwita ya ce wannan ne karo na takwas kuma na ƙarshe da Buhari ke halartar wannan biki a matsayinsa na shugaban ƙasa.
Daga cikin waɗanda suka halarci bikin wanda aka gudanar a Abuja babban birnin ƙasar sun haɗar da mataimakin shugaban ƙasar Farfesa Yemi Osinbajo da shugaban majalisar dattawan ƙasar Sanata Ahmad Lawan da kakakin majalisar wakilai Femi Gbajabiamila da babban alƙalin alƙalan ƙasar, Mai shari’a Olukayode Ariwoola, da sauran manyan jami’an gwamnati.
Ana dai gudanar da wannan biki ne a duk shekara domin tunawa da irin gagarumar gudunmowar da tsoffin dakarun ƙasar suka bayar wajen zaman lafiya da ci gaban ƙasar.
A wajen bikin Shugaban ƙasar da sauran jami’an gwamnati kan ajiye furanni domin nuna jinjina ga ‘yan mazan jiyan, tare da yin faretin girmama wa ga shugaban ƙasa, sannan kuma shugaban ya saki fararen tattabaru suka tashi sama duk domin nuna tunawa da irin ƙwazon da ‘yan mazan jiyan suna nuna ga ƙasar.