Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya gargadi sabon kwamitin ayyuka na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na kasa cewa, kada su bari ‘yan takara mafi karfin arziki su rinjaye su a zaben fidda gwani na jam’iyyar.
Buhari ya yi wannan gargadin ne a babban taron jam’iyyar APC na kasa a shekarar 2022 da aka gudanar a Abuja, inda ya bukaci shugabannin jam’iyyar da su rika inganta dimokuradiyyar cikin gida a kodayaushe da kuma daidaito ga dukkan ‘ya’yan jam’iyyar.
Ya yi kira ga ‘yan siyasa da masu zabe da su inganta tsarin zabe, su kara nuna gaskiya, cike gibin da ake da su, sannan su kara kima ga dimokradiyyar Najeriya, domin dimokuradiyyar ta samu ci gaba.
Shugaban wanda ya bayyana dalilansa na sa baki a cikin al’amuran jam’iyyar a kwanakin baya, ya ce ba wai an yi hakan ne don danne muryoyin da ba su dace ba.
“Kwanan nan, na sami dalilin shiga cikin rikicin shugabancin da ke shirin kawo rudani a cikin jam’iyyar.Irin wadannan rigingimun cikin gida sun zama ruwan dare a cikin dimokuradiyya irin namu, amma dole ne mu guji zafafa harkokin siyasa, kada mu bari bambance-bambancen da ke tsakaninmu ya tsaga da kawo cikas ga jam’iyyar.
“Kamar yadda na fada a baya, ba ta amfanar kowa ko jam’iyya, idan mu a matsayinmu na shugabanni muka yi kasa a gwiwa, muka koma ga bata-kashi da suna a kafafen yada labarai. In ji Buhari.