Jim kadan bayan dawowarsa daga jihar Ebonyi, shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya gana da wasu gwamnonin Arewa da kuma shugabannin hukumomin tsaro a fadar shugaban kasa ta Villa Abuja.
Taron wanda ya gudana a bayan fage a zauren majalisar na fadar shugaban kasa, an fara shi ne da misalin karfe uku na rana.
Ba a bayar da cikakken bayani kan dalilan ganawar ba, sai dai majiyoyi daga fadar shugaban kasar sun ce, taron na da alaka da matsalar tsaro a kasar nan, musamman a Arewacin kasar nan.
Daga cikin gwamnonin da suka halarci taron akwai Simon Lalong na Filato, Nasir El-Rufa’i na Kaduna, Abdullahi Ganduje na Kano, Aminu Tambuwal na Sokoto, Sani Bello na Niger, Abubakar Badaru na Jigawa, Umara Zulum na Borno, Atiku Bagudu na Kebbi da Bello Matawalle na Zamfara.
An tattaro cewa, duka gwamnonin Katsina da Yobe, Bello Masari da Mai Mala Buni, su ma ana sa ran halartar su a wajen.
Har ila yau, Ministan Tsaro, Manjo Janar Bashir Magashi mai ritaya ya jagoranci tawagar tsaro, ciki har da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro (NSA), Manjo Janar Babagana Monguno mai ritaya; babban hafsan hafsoshin tsaro, Janar Lucky Irabor; hafsoshin tsaro da shugabannin sauran hukumomin tsaro sun halarci taron.
Hafsan hafsoshin da suka halarci taron sun hada da babban hafsan soji, Laftanar Janar Farouk Yahaya; Babban Hafsan Sojin Ruwa, Vice Admiral Awwal Gambo; da Shugaban Hafsan Sojan Sama, Air Marshal Isiaka Oladayo Amao.
Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da Sufeto-Janar na ‘yan sanda, Alkali Baba Usman; Babban Darakta Janar na Hukumar Tsaro ta farin kaya (DSS), Yusuf Bichi; da Darakta-Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa (NIA), Ahmed Rufa’i Abubakar.