fidelitybank

Buhari ya gana da gwamnonin Arewa a kan matsalar tsaro

Date:

Jim kadan bayan dawowarsa daga jihar Ebonyi, shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya gana da wasu gwamnonin Arewa da kuma shugabannin hukumomin tsaro a fadar shugaban kasa ta Villa Abuja.

Taron wanda ya gudana a bayan fage a zauren majalisar na fadar shugaban kasa, an fara shi ne da misalin karfe uku na rana.

Ba a bayar da cikakken bayani kan dalilan ganawar ba, sai dai majiyoyi daga fadar shugaban kasar sun ce, taron na da alaka da matsalar tsaro a kasar nan, musamman a Arewacin kasar nan.

Daga cikin gwamnonin da suka halarci taron akwai Simon Lalong na Filato, Nasir El-Rufa’i na Kaduna, Abdullahi Ganduje na Kano, Aminu Tambuwal na Sokoto, Sani Bello na Niger, Abubakar Badaru na Jigawa, Umara Zulum na Borno, Atiku Bagudu na Kebbi da Bello Matawalle na Zamfara.

An tattaro cewa, duka gwamnonin Katsina da Yobe, Bello Masari da Mai Mala Buni, su ma ana sa ran halartar su a wajen.

Har ila yau, Ministan Tsaro, Manjo Janar Bashir Magashi mai ritaya ya jagoranci tawagar tsaro, ciki har da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro (NSA), Manjo Janar Babagana Monguno mai ritaya; babban hafsan hafsoshin tsaro, Janar Lucky Irabor; hafsoshin tsaro da shugabannin sauran hukumomin tsaro sun halarci taron.

Hafsan hafsoshin da suka halarci taron sun hada da babban hafsan soji, Laftanar Janar Farouk Yahaya; Babban Hafsan Sojin Ruwa, Vice Admiral Awwal Gambo; da Shugaban Hafsan Sojan Sama, Air Marshal Isiaka Oladayo Amao.

Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da Sufeto-Janar na ‘yan sanda, Alkali Baba Usman; Babban Darakta Janar na Hukumar Tsaro ta farin kaya (DSS), Yusuf Bichi; da Darakta-Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa (NIA), Ahmed Rufa’i Abubakar.

sunnnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...

Ni da Wike tif da taya ne – Fubara

Dakataccen gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya ce, babu...

Za a yi jana’izar Dantata a ranar Litinin

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid,...

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaÉ“en 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin É—an kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...
X whatsapp