fidelitybank

Buhari ya gabatar da kasafin ƙarshe a Majalisa

Date:

Shugaba Muhammadu Buhari, ya gabatar da kasafin kuɗi na 2023 da ya kai naira tiriliyan 19.76 a gaban gamayyar majalisun dokokin kasar ranar Juma’a.

Kasafin shi ne na ƙarshe da shugaban ya gabatar yayin da yake shirin kammala wa’adin mulkinsa na biyu a ranar 29 ga watan Mayun 2023, yana mai cewa “ina son na bar abin tarihi a kasar fiye da yadda na same ta a 2015”.

Wannan ne kasafin kuɗi mafi yawa a tarihin Najeriya, inda ya zarta na shekarar 2022 da kashi 15.37 – wanda aka gabatar kan naira tiriliyan 17.13.

Kasafin kuɗin yana da giɓin da sai gwamnati ta hada da rance za ta cike fiye da rabin sa, wanda ya kai tiriliyan 12.

Ministar Kuɗi Zainab Shamsuna ta ce gwamnati za ta cike gɓin ne ta hanyar ciyo bashi da kuma sayar da wasu kadarorin gwamnati.

Kazalika akwai batun tallafin man fetur, wanda shi ma ƙarin dawainiya ne ga kasafin, wanda zai iya janyo zazzafar muhawara, kasancewar wasu na goyon bayan gwamnati ta ci gaba da ba da shi, yayin da wasu ke ganin ya kamata a dakatar, saboda a nasu ra’ayin masu hada-hadar man sun fi talaka cin gajiyar tallafin.

Sai dai ƴan majalisar da dama na da ra’ayin cewa akwai bukatar a jira a ga gangariyar abin da kasafin ya kunsa.

Honarabul  Jafar Sulaiman Ribadu, ɗan majalisar wakilai ne daga Jihar Adamawa wanda ke cewa zai so su karbi kudirin kasafin kudin da zuciya daya.

Amma Sanata Adamu Muhammad Bulkachuwa ya tabbatar da cewa an samu cikas wurin aiwatar da kasafin kuɗin bana a wasu ɓangarorin saboda rashin samun isassun kuɗin da za a aiwatar da shi.

Sai dai ya ce ana sa ran kafin ƙarshen shekara za a samu shigowar wasu kuɗin da za a ci gaba da ayyuka.

Za a iya cewa zumuɗi da ɗokin sauraron kasafin kuɗin na shekara-shekara ya ragu a tsakanin ‘yan Najeriya da dama, sakamakon yanke ƙaunar da wasu ke yi suna zargin cewa da yawa faɗa ne kawai ba cikawa.

taraba state today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...

Sojoji sun kashe rikaken dan Bindiga Dan Dari Biyar a Sokoto

Dakarun Operation FANSAR YANMA sun yi nasarar fatattakar wani...

An kashe utane 30 a yakin Thailand da Cambodia

An shiga kwana na uku na faɗan kan iyaka...

Ba mu ƙayyade shekarun shiga ƙaramar sakandare JSS1 – Ma’aikatar Ilimi

Ma'aikatar Ilimi a Najeriya ta musanta rahoton da wasu...

Ido da Ido na ga yadda Sojojin Isra’ila ke kashe Falasdinawa – Tsohon Sojin Amurka

Wani tsohon sojan Amurk ya ce, ya ga yadda...

‘Yan majalisar Birtaniya 220 na neman ƙasar ta amice da ƙasar Falasɗinu

'Yan majalisar Birtaniya 220 sun nemi gwamnatin ƙasar ta...

Buhari yaki karbar kyautar Agogon lu’u-lu’u da jirgin sama – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Najeriya Muhammad Buhari,...

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...
X whatsapp