Kungiyar malaman jami’o’i ta kasa ASUU ta nuna shakkunta game da kin cika alkawuran da gwamnatin shugaba Buhari ta dauka na samar da mafita ga matsalolin da fannin ilimin kasar ke ciki.
Kungiyar ta ce, za ta fara yajin aikin sai baba ta gani nan ba da jimawa ba.
A wata sanarwa da ta fitar a ranar Juma’a, ASUU ta nuna fushinta kan yadda aka rinka zaman sasanci tsakaninta da gwamnati kan yadda za a farfado da ilimi, sai dai gwamnati ta gaza cika alkawarin ta, abin da take ta ikirari a baya.
Kungiyar ta bayyana lamarin da ke faruwa a halin yanzu da “Abin kunya” yadda gwamnatin tarayya ke ci gaba da kare tsarin biyan kudi na IPPIS, duk da zargin cewa, akwai almundahana a cikinsa, kamar yadda ya bayyana a cikin rahoton da babban akantan tarayya ya gabatar a gaban Majalisar dattawa.