Shugaban kasa Muhammadu Buhari da yammacin ranar Asabar ya dawo Abuja, bayan ziyarar kwanaki biyu da ya kai babban birnin kasar Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), Abu Dhabi
Buhari ya bar Najeriya ne a ranar Alhamis, kuma ya sauka a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja ranar Asabar da misalin karfe 4 na yamma, tare da ‘yan tawagarsa.
A yayin da ya ke birnin Abu Dhabi, shugaba Buhari ya gana da sabon shugaban Hadaddiyar Daular Larabawa, Mai Martaba Sheikh Mohamed bin Zayed Al Nahyan, inda ya mika ta’aziyyar sa da na Najeriya game da rasuwar tsohon shugaban kasa kuma Sarkin Abu Dhabi, mai martaba Sheikh Khalifa. bin Zayed Al Nahyan.