Jigo kuma wanda ya kafa Jamiāar Afe Babalola, AdoEkiti (ABUAD), Aare Afe Babalola, ya shawarci Gwamnatin Tarayya da ta dakatar da zaben 2023 tare da ba da damar kafa gwamnatin rikon kwarya ta watanni shida bayan mulkin Shugaba Muhammadu Buhari, wanda zai samar da sabon kundin tsarin mulki, domin magance matsalolin tsaro, tattalin arziki, siyasa da sauran munanan cututtuka da suka addabi al’umma.
Babalola ya shaida wa taron manema labarai a Ado-Ekiti ranar Litinin cewa, kamata ya yi gwamnatin rikon kwarya ta kasance a ofis, don tsara wani sabon tsari ga Najeriya.
Ya jaddada cewa, ya kamata a dakatar da zabukan 2023 har sai Najeriya ta samu ātsarin mulkin jamaāa wanda zai tanadi āyan majalisa na wucin gadi da kuma wadanda ba shugaban kasa ba.ā
Babalola ya ce, ya kamata a zabo mambobin gwamnatin rikon kwarya daga dukkan tsoffin shugabannin kasa da mataimakansu; wasu zababbun ministoci da gwamnoni da wakilan manyan kungiyoyin kwararru.