fidelitybank

Buhari ya bar Emefiele ya ci karansa babu babbaka – Gwamnatin Tarayya

Date:

Fadar shugaban Najeriya ta ce yawancin kuɗaɗen da aka fitar daga Babban bankin ƙasar (CBN) ƙarƙashin shugabancin Godwin Emefiele, an fitar da su ne ba tare da sa hannun tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ba.

Ajuri Ngelale, mashawarci na musamman ga shugaban ƙasa Bola Tinubu kan harkokin yaɗa labarai da wayar da kan jama’a ne ya bayyana hakan a wata hira da ya yi a shirin With Chude na Chude Jideonwo wanda aka watsa a gidan talabijin na Channels.

Ngelale ya ce dole ne gwamnatin da ta gabata ta ɗauki alhakin wasu abubuwan da suka faru a babban bankin ƙarƙashin jagorancin Emefiele.

Ngelale ya jaddada cewa, yayin da Buhari ya samu nasarori a wasu fannonin samar da ababen more rayuwa, rashin sanya ido kan al’amuran Babban bankin ya taimaka wajen taɓarɓarewar tattalin arziƙin ƙasar.

Duk da cewa ya amince cewar Bola Tinubu ya bai wa gwamnati tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari goyon baya, Ngelale ya ce a yanzu Tinubu na ƙoƙarin ganin ya magance matsalolin da suka haifar da taɓarɓarewar tattalin arzikin kasar da ta faru a zamanin gwamnatin Buhari.

Ngelale ya yi nuni da cewa Buhari ne ya yanke shawara dangane da tsawaita wa’adin mulkin Emefiele, duk kuwa da cewa shugaban bai san al’amuran da ke gudana a Babban Bankin ba.

Ngelale ya bayar da misali da yadda Babban Bankin ya fitar da kuɗi dalar Amurka miliyan 6.2 ga masu sa ido kan zaɓuka daga ƙasashen waje, wanda aka ce da sa hannun Buhari ne, inda daga baya aka yi zargin jabu ne.

Emefiele, wanda shugaban kasa Goodluck Jonathan ya naɗa tun farko, ya ci gaba da zama gwamnan CBN a gwamnatin Buhari.

Sai dai kuma ya fuskanci shari’a a watan Yunin da ya gabata kan wasu tuhume-tuhume na cin hanci da rashawa da suka hada da na sa hannun bogi da kuma karbar kudi ta hanyar ƙarya.

nnn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp