Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da nadin Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero a matsayin Uban jami’ar Calabar ta jihar Cross River.
Shugaban Jami’ar, Janar Matthew Luther Agwai mai ritaya ne ya bayyana hakan, a ranar Laraba, a lokacin da ya jagoranci ‘yan majalisar zuwa ziyarar taya murna da suka kai wa Sarkin a fadarsa.
Agwai ya ce”Al’ummar Jama’ar Calabar ta cika da murna da nadin da a ka yi wa Sarki Aminu Ado Bayero a matsayin sabon Uban Jami’ar. Dimbin gogewar Sarkin, jami’ar za ta samu babban matsayi na ilimi”.
Da ya ke mayar da martani, Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero ya nuna jin dadinsa ga gwamnatin tarayya da ta same shi da ya cancanci zama Uban Jami’ar.
“Muna tattaunawa da jami’ar Calabar da ke jihar Cross River, kuma za mu yi iya kokarinmu wajen ganin an samu nagartaccen Ilimi.” A cewar Alhaji Aminu Ado Bayero.
Sarkin ya nemi goyon bayan daukacin ‘yan Majalisar da na Jami’ar wajen ganin an cimma burin da a ke so.
Daga nan sai ya yaba da namijin kokarin da Shugaban Jami’ar, Janar Matthew Luther Agwai, da ‘yan uwa na Jami’ar su ka yi, inda ya bukace su da su ci gaba da gudanar da aikin.