fidelitybank

Buhari ya amince da nada Sarkin Kano a matsayin Uban Jami’a

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da nadin Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero a matsayin Uban jami’ar Calabar ta jihar Cross River.

Shugaban Jami’ar, Janar Matthew Luther Agwai mai ritaya ne ya bayyana hakan, a ranar Laraba, a lokacin da ya jagoranci ‘yan majalisar zuwa ziyarar taya murna da suka kai wa Sarkin a fadarsa.

Agwai ya ce”Al’ummar Jama’ar Calabar ta cika da murna da nadin da a ka yi wa Sarki Aminu Ado Bayero a matsayin sabon Uban Jami’ar. Dimbin gogewar Sarkin, jami’ar za ta samu babban matsayi na ilimi”.

Da ya ke mayar da martani, Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero ya nuna jin dadinsa ga gwamnatin tarayya da ta same shi da ya cancanci zama Uban Jami’ar.

“Muna tattaunawa da jami’ar Calabar da ke jihar Cross River, kuma za mu yi iya kokarinmu wajen ganin an samu nagartaccen Ilimi.” A cewar Alhaji Aminu Ado Bayero.

Sarkin ya nemi goyon bayan daukacin ‘yan Majalisar da na Jami’ar wajen ganin an cimma burin da a ke so.

Daga nan sai ya yaba da namijin kokarin da Shugaban Jami’ar, Janar Matthew Luther Agwai, da ‘yan uwa na Jami’ar su ka yi, inda ya bukace su da su ci gaba da gudanar da aikin.

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp