Wani dattijo kuma babban lauya, Robert Clarke, SAN, a ranar Litinin a Abuja, ya ce, shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya kamata ya yi wa’adin karin watanni shida, domin ya ba shi isasshen lokaci don magance matsalolin tsaron kasar.
Clarke ya bayyana cewa, kasa da shekara guda kafin zaben 2023, babu isasshen lokacin da za a magance matsalar rashin tsaro don tabbatar da an gudanar da aikin lafiya.
Da yake magana a shirin talabijin na Arise, ya bayyana cewa, kundin tsarin mulkin kasar ya ba wa shugaban kasa damar kara wa’adinsa na tsawon watanni shida a matakin farko idan har ba a cika sharuddan zabe ba.
Sai dai ya yi gargadin cewa, al’ummar kasar ba za ta iya kaiwa 2023 ba, idan ba a yi wani abu ba kafin zaben.