Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya amince da inganta Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya da ke Yola, zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Modibbo Adama da ke Yola a Jihar Adamawa.
An bayyana amincewar ne ga manema labarai a cikin wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai na Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya (OSGF), Mista Willie Bassey ya fitar a jiya.
Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Yin amincewa da bukatar da jama’a da gwamnatin Jihar Adamawa suka yi na inganta Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya da ke Yola zuwa, Asibitin Koyarwa na Jami’ar Modibbo Adama da ke Yola, domin inganta horas da daliban Likitan kamar yadda ya kamata. tare da inganta harkokin kiwon lafiya a jihar”.
Har ila yau, Shugaba Buhari ya ba da izinin sabunta nadin Darakta-Janar Babban Jami’in Cibiyar Bincike da Cigaban Magunguna ta Kasa (NIPRD), Dakta Obi Peter Odigwe, na wa’adi na biyu kuma na karshe na shekaru hudu daga aiki.